in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta rufe kan iyakoki daga 26 zuwa 28 ga wata dalilin zabe
2015-03-26 10:26:50 cri

Kasar Najeriya ta rufe kan iyakokinta na kasa da na ruwa tun daga ranar 26 har zuwa 28 ga watan Maris dalilin zabukan da za su gudana, in ji hukumar kula da harkokin shige da fice ta kasar Najeriya (NIS) a ranar Laraba.

David Parradang, babban mai sa ido a hukumar NIS, ya kuma bukaci 'yan kasashen waje dake zaune a Najeriya, musammun ma wadanda suka fito daga kasashe makwabta kamar su Kamaru, Nijar da Chadi da su kiyaye shiga harkokin zabuka.

Zaben shugaban kasar Najeriya zai gudana a ranar 28 ga watan Maris, kafin zaben gwamnoni da na 'yan majalisu da aka tsaida shiryawa a ranar 11 ga watan Afrilu. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China