in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya taya murnar bude bikin nune-nunen fasahohin sadarwa na Hannover na shekarar 2015 a kasar Jamus ta hanyar bidiyo
2015-03-16 15:38:02 cri
An bude bikin nune-nunen fasahohin sadarwa na Hannover na shekarar 2015 a birnin Hannover dake kasar Jamus a ranar 15 ga wata da dare. Kasar Sin na daga cikin kasashen dake halartar bikin baje kolin a wannan karo cikin hadin gwiwa. Saboda haka firaministan kasar Sin Li Keqiang ya taya murnar budewar bikin ta hanyar bidiyo, kuma shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta halarci bikin bude baje kolin.

A cikin jawabinsa, Li Keqiang ya bayyana cewa, yanzu an fara yin kwaskwarima kan fasahohin zamani a wani sabon zagaye, inda kasashe da dama sun gabatar da manufofinsu kan inganta fasahohin zamani. Gwamnatin kasar Sin ta yi la'akari da halin da ake ciki a kasarta da matakin bunkasuwarta a halin yanzu, ta gabatar da wani shiri mai taken 'Aikin kera kayayyaki a kasar Sin a shekarar 2025' a matsayin hanyar raya sha'anin kera kaya na kasar Sin a shekaru 10 masu zuwa. Kana za a fadada hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Jamus a fannonin yanar gizo, sadarwa da dai sauransu.

A nata bangare, shugabar gwamnatin Jamus Merkel ta nuna godiya ga Li Keqiang da ya nuna kyakkyawan fata ga bikin nune-nunen a wannan karo, kuma ta bayyana cewa, kasar Sin abokiyar kasar Jamus ce mafi girma a fannin ciniki a nahiyar Asiya, kana ita ce muhimmiyar abokiyar hadin gwiwa a fannin nazarin fasahohin zamani. Ta ce, Jamus da Sin suna da fifiko a fannin tattalin arzikin sadarwa, don haka kasashen biyu za su iya yin hadin gwiwa da samun moriyar juna a wannan fanni. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China