in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Sudan ya ce zai yi murabus in har ba'a sake zaben shi ba
2015-02-27 10:55:05 cri

Shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir ya ce, zai yi murabus har al'ummar kasar ta bukaci hakan, ta kin sake zaben shi a babban zaben dake tafe.

Al-Bashir, 'dan takara a jam'iyyar dake mulkin kasar National Congress Party NCP, a ranar Alhamis din nan ya kaddamar da yakin neman zaben shi daga Medani a jihar Gezira, inda yake neman sake darewa karagar mulkin kasar a karo na uku.

Dubban magoya bayan shugaban da jam'iyyar sun taru a dandalin birnin Medani dauke da alluna da kyallewa dake nuna goyon bayansu ga shugaban kasar al-Bashir.

Shi dai shugaba al-Bashir ya sake nanata kiran shi ga tattaunawa ta kasa, a inda ya ce, har yanzu suna kira ga 'yan adawa da masu dauke da makamai da su kawo bukatunsu a kan teburin shawarwari su kuma mutunta ra'ayin masu rinjaye, domin wannan shi ne demokradiya. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China