in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za'a ci gaba da tattaunawar samar da zaman lumana a Libya
2015-02-10 10:38:28 cri

Tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD dake kasar Libya UNSMIL ta bayyana cewar, a mako mai zuwa ne kungiyoyi masu fada da juna za su koma bisa teburin tattaunawa domin kaiwa ga samar da zaman lafiya a kasar, wacce ta fada cikin yaki tun bayan rasuwar tsohon shugaban kasar Muammar Gaddafi.

Za'a gudanar da tattaunawar zaman lafiyar a karkashin shiga tsakani na MDD, wacce ita ce ta yi sular samar da tattaunawar sulhu tsakanin sassan biyu.

Wata sanarwa tawagar MDD ta ce, da za ran an kammala shirye-shiryen taron da samar da matakan tsaro, za'a sanar da dandalin da za'a gudanar da taron da kuma takamaiman lokacin taron.

Sanarwar ta ce, a mako mai zuwa za kuma a gudanar da wani makamancin taron tattaunawa a Geneva dake Switzerland a inda daukacin jam'iyyun siyasa da masu kare hakkin bil'adama na kasar Libya za su hallara.

Sanarwar ta ce, za kuma a gudanar da wani taron wanda zai kunshi kwamandojin kungiyoyin dake fada da juna domin shirya su tunkarar taron samar da zaman lafiyar da za'a yi.

Taron wanzar da zaman lumana a Libya yana da muradin kaiwa ga yarjejeniyar yadda za'a tafiyar da canjin siyasa a Libya, tare da kafa gwamnatin hadin gwiwa da kuma kawo karshen fadace-fadacen da ake fama da su a sassa dabam-dabam na kasar. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China