in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamaru za ta shirya taro domin tattaunawa kan barazanar Boko Haram
2015-02-04 14:33:58 cri

Kasar Kamaru za ta zamanto mai masaukin baki na taron kungiyar tattalin arzikin kasashen Afrika ta tsakiya domin tattaunawa a kan yaki da 'yan kungiyar tsagera ta Boko Haram na Nigeria.

Shugabannin yankunan dabam-dabam na Afrika sun amince da gudanar da wannan taro a ranar 16 ga watan Fabarairun da muke ciki a lokacin taron kolin kungiyar hadin kan Afrika wanda aka yi kwanan nan a Habasha.

A yayin taron kolin kungiyar hadin kan kasashen Afrika, shugabannin sun duba barazanar kungiyar Boko Haram a kasasr Nigeria da kuma kasashe makwabta.

Taron ya jinjinawa shugaban Kamaru Paul Biya saboda yakin da yake yi da 'yan kungiyar ta Boko Haram a kasasrsa.

Hakazalika taron ya yabawa nasarorin da dakarun kasar Chadi suka samu a yakin da suke yi da 'ya'yan kungiyar tun bayan da aka tura su kasar Kamaru a tsakiyar watan Janairu.

Taron shugabannin kasashen AU ya kuma amince da samar da wasu kudurorin tsaro na yankin Afrika ta yamma domin marawa Kamaru da Chadi baya a kokarin da suke yi na yaki da kungiyar Boko Haram.

A watan da ya gabata ne kungiyar ta AU a karkashin kwamitinta na tsaro da zaman lafiya ta kirkiro da wata rundunar hadin gwiwa ta dakaru 7,500 domin yaki da kungiyar Boko Haram. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China