Kotun hukunta manyan laifuffuka ta kasa da kasa game da kasar Rwanda (TPIR), dake da cibiya a birnin Arusha na kasar Tanzaniya, za ta dakatar da ayyukanta a cikin watan Satumba mai zuwa, bayan ta kwashe kusan shekaru ashirin tana gurfanar a gaban kotu wadanda ke da hannun tsamo tsamo a cikin kisan kiyashin shekarar 1994 a kasar Rwanda, yakin basasan da ya hallaka fararen hula kusan miliyan guda da ba su ji ba su gani ba.
Bisa shirye shiryen wannan rufewa, kotun ta sallami a baya bayan nan ma'aikatansa 117 daga 414, in ji jami'in TPIR mai kula da hulda da jama'a, Danford Mpumilwa a ranar Talata a cikin wata sanarwa. (Maman Ada)