Wasu mata biyu dauke da gurmeti da wasu nakiyoyi masu fashewa, sun shiga hannun jami'an tsaro a ranar Litinin a Toubia, wani yankin kasar Chadi dake kusa da birnin N'Djamena, bayan sun ratso kasar Kamaru a yayin da suka fito daga Najeriya a jajibirin karbe garin Gambaru da sojojin Najeriya suka yi daga hannun Boko Haram tare da taimakon sojojin kasar Chadi, a wani labarin da Xinhua ya samu daga wata mijiyar tsaro a ranar Talata da safe.
Matan biyu suna da niyyar tada nakiyoyin nasu a N'Djamena, babban birnin kasar Chadi. Matan dai na dauke da wadannan nakiyoyin da aka sanya cikin bududuwan da ake yanke, sannan aka rufe wayar karfe, domin a yi tsammanin suna dauke da madara, in ji wannan majiya ta wayar tarho. (Maman Ada)