in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Chadi ta karbi kujerar shugabancin kwamitin tsaron MDD na Disamba
2014-12-02 10:22:17 cri

Kasar Chadi a ranar Litinin din nan ta karbi shugabancin kwamitin tsaro na MDD na watan Disamba. Cherif Mahamat Zene, wakilin din din din na kasar a majalissar ya karbi shugabancin kwamitin ne ake yi zagaye zagaye daga wajen Gary Quinlan, jakadan kasar Australiya a majalissar wanda ya rike kujerar a watan Nuwamba.

A matsayin kasar da ba ta da kujerar din din din a kwamitin, Chadi ta fara wa'adinta na shekaru biyu a kwamitin mai wakilai 15 a ranar 1 ga watan Janairun wannan shekarar ta 2014.

Kamar yadda tsarin majalissar yake, kwamitin tsaron ke da nauyin tafiyar da ayyukan zaman lafiya da tsaro a duniya baki daya, yana da wakilan din din din guda 5 da suka hada da kasashen Sin, Amurka, Britaniya, Faransa da Rasha. Sai kuma wakilai da ba na din din din ba guda 10 da aka zabe daga shekaru 2 zuwa 5.

Shugabancin kwamitin, ana yin shi ne zagaye zagaye a tsakanin kasashen dake cikin kwamitin tsaro da wanzar da zaman lafiya duk wata, bisa farkon kalmar sunan kasa a haruffan Turanci. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China