A kasar Chadi, kimanin mutane miliyan uku ne za su bukaci taimakon jin kai a shekarar mai zuwa a wannan kasa da matsalar jin kai ke tabarbarewa sakamakon rikice rikice masu sarkakiya dake faruwa a kai a kai, in ji madam Magda Verdickt, jami'ar dake kula da harkokin jin kai a cibiyar tsarin ayyukan MDD dake kasar Chadi.
A shekarar 2015, mutane miliyan 2,4 ne za su fuskanci matsalar karancin abinci, kana kananan yara fiye da dubu dari uku da hamsin dake fama da rashin abinci mai gina jiki ne za su bukaci taimakon jin kai, in ji madam Verdickt. (Maman Ada)