in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyoyi dake fada da juna a Sudan ta Kudu sun amince da yarjejeniyar tsagaita wuta
2015-02-03 12:49:45 cri

Shugaban kasar Sudan ta Kudu Salva Kiir da tsohon mataimakinsa Riek Machar sun rattaba hannu a kan wata yarjejeniya sulhu ta dakatar da fadan da ake tafkawa a kasar.

An dai samu damar tattaunawa ne tsakanin shugaban kasar da tsohon mataimakinsa a karkashin shiga tsakani na IGAD, kuma an sa hannun kan yarjejeniyar ne domin kawo karshen yakin da ya barke a watan Disambar shekarar 2013.

Kundin yarjejeniyar ya bayar da tabbacin girka gwamnatin rikon kwarya ta hadin kan kasa tare da kafa hukumomi na wucin gadi na shari'a da kuma matakai na sa ido a kan lamurra.

Firaministan kasar Ethiopia Hailemariam Dessalegn ya bukaci sassan biyu da su girmama yarjejeniyar da suka rattaba hannu a kai.

Wakili na musamman na shugaban kungiyar IGAD a Sudan ta Kudu Eyoum Mesfin ya ce, za'a kammala tattaunawa a kan yarjejeniyar lumana tsakanin sassan biyu a ranar 20 ga watan Fabarairu da muke ciki domin girka cikakken tsari na zaman lafiya, ko kafin ranar 5 ga watan Maris. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China