Kwamitin tsaron MDD ya fidda wata sanarwa, dake Allah wadai da karuwar hare-haren ta'addanci daga mayakan kungiyar Boko Haram, yana mai cewa, fitinar da mayakan kungiyar ke haddasawa a Najeriya da sauran kasashe makwaftanta, na barazana ga zaman lafiyar daukacin nahiyar Afirka.
Sanarwar ta bayyana harin baya bayan nan da mayakan suka kai, a yunkurinsu na shiga birnin Maiduguri, fadar gwamnatin Borno, da sauran hare-hare kan garuruwan dake yankin tafkin Chadi, a matsayin abin takaici.
Daga nan sai kwamitin tsaron ya jaddada kira ga mahukuntan yankunan da ke fuskantar barazana daga Boko Haram, da su hada gwiwa wajen daukar karin matakan murkushe kungiyar.
Bugu da kari kwamitin tsaron MDDr ya jaddada aniyarsa ta ci gaba da yaki, da dukkanin nau'o'in ayyukan ta'addanci, tare da gurfanar da masu aikata su gaban kuliya. (Saminu)