in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Kamaru da Chadi na ci gaba da fafatawa da mayakan Boko Haram a arewacin Kamaru
2015-02-02 10:46:16 cri

Kazamin fada na ci gaba da gudana tsakanin sojojin Kamaru da na kasar Chadi da mayakan kungiyar Boko Haram ta Najeriya a ranar Lahadi da yamma fiye da sa'o'i uku a Fotokol, wani yankin dake kuriyar arewacin Kamaru dake iyaka da Najeriya, a cewar wasu majiyoyin sojan kasar Kamaru.

Ranar daya ga watan Febrairu, rana ce da ta fi kasancewa cikin rudani ga Boko Haram, wanda bayan wani harin da ta kai da bai ci nasara a muhimmin yankin Maiduguri dake arewa maso gabashin Najeriya, da kuma hare hare ta sama na sojojin kasar Chadi a Gambaru na wannan yankin, dakarun na Boko haram ba su farga ba na kai hare hare a Fotokol dake kasar Kamaru, inda musanyar wuta ta fi kazancewa tun da yammacin ranar, a cewar wasu majiyoyi ba tare da ba da wani adadi ba. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China