Babban sakataren kasar Amurka John Kerry ya bayyana a ranar Lahadi a birnin Lagos cewa, gwamnatin Amurka na iyar kai ga hana takardar Visa ga wadanda ke rura wutar siyasa da tashe tashen hankalin siyasa a Najeriya. Muna son mu gaya wa duk 'dan Najeriyar da ya yi kokarin tada duk wani nau'in tashe tashen hankali a lokacin zabuka, to ba zai iya samun visan Amurka ba, in ji Kerry a yayin wani taron manema labarai bayan wata ganarwarsa tare da shugaban mai barin gado Goodluck Jonathan da kuma janar mai ritaya Muhammadu Buhari 'dan takarar jam'iyyar adawa ta APC. (Maman Ada)