in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Botswana ta yabawa tawagar ma'aikatan lafiya na kasar Sin
2015-01-23 10:07:02 cri

Ma'aikatar lafiya ta kasar Botswana ta yaba da irin gudumawar da tawagar ma'aikatan lafiya ta kasar Sin da ke aiki a kasar suka bayar.

Ministar lafiyar kasar Botswana Dorcas Makgato ce ta bayyana hakan yayin wata liyafar ban-kwana da aka shiryawa rukuni na 13 na tawagar ma'aikatan lafiyar kasar Sin da ke Botswana, don nuna godiya kan irin gudummawar da suka ba da a lokacin da suke aiki a asibitin ginbiya Marina da ke Gaborone da kuma asibitin Nyangabgwe a Francistown, birni na biyu mafi girma a kasar ta Botswana.

Madam Dorcas ta ce, a shekarar 1985 ne rukuni na farko na ma'aikatan lafiyar kasar Sin ya fara aiki a kasar Botswana da ma'aikata 13, inda adadin ya karu zuwa 46, lamarin da ke nuna ingantuwar dangantaka tsakanin Sin da kasar Botswana.

Shi ma da yake jawabi, jakadan Sin a kasar Botswana Zheng Zhuqiang ya ce, bangaren kula da lafiyar al'umma, shi ne muhimmin sashin hadin gwiwa tsakanin sassan biyu.

A karshen liyafar, ministar lafiyar kasar Botswana ta baiwa dukkan ma'aikatan lafiyar kasar Sin lambar yabo saboda abin da ta kira gagarumar gudumawar da suka baiwa kasarta. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China