in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za'a gudanar da zaben Cote d'Ivoire a kan lokaci
2015-01-16 10:16:04 cri

Wani babban jami'in hukumar zaben kasar Cote d'Ivoire ya ba da tabbacin cewar, za'a gudanar da zaben shugaban kasa na kasar a watan Oktobar wannan shekarar kamar yadda aka tsara.

Babban jami'in hukumar zabe ta kasar Sourou Kone ya bayar da wannan tabbacin ne jim kadan bayan ganawarsa da sabon wakili a kan yancin 'dan adam a kasar ta Cote d'Ivoire na MDD Mohammed Ayat.

Kone ya ce, za'a dauki dukanin matakin da ya dace domin tabbatar da cewar, duk 'dan kasar da ya isa kada kuri'a ya samu damar jefa kuri'arsa a lokacin zaben.

Kone ya kara da cewar, wakilin na MDD ya nuna gamsuwarsa game da matakan da kasar ta dauka na gudanar da zabe.

Zaben na Oktoba ana ganin zai taimaka wajen samar da kwanciyar hankali a kasar bayan da kasar ta fada cikin mummunan rikici a karshen zaben shekarar 2010 zuwa 2011. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China