in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Nigeriya sun hallaka mayakan Boko Harom 78 a cikin arangama
2015-01-16 09:29:22 cri

Sojojin Nigeriya a jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar sun tabbabar da hallaka mayakan Boko Haram 78 a lokacin wata arangama da suka yi bayan da mayakan suka yi kokarin shiga garin Biu.

Wata majiyar tsaro mai tushe ta shaida wa Xinhua cewa, da sanyin safiyar Laraba ne lamarin ya faru, a cikin wadanda aka hallaka, har da wassu 'yan kasashen waje, sannan an damke wasunsu, a kalla an kirga gawawwaki 78 na mayakan, in ji wannan majiya.

Ya ce, an samu manyan bindigogin harbar jiragen sama guda biyu daga hannun mayakan a lokacin arangamar. Yana mai bayanin cewa, an yi dauki ba dadi sosai tsakanin sojojin Nigeriya da wadannan mayakan kafin su samu kwato ikon jihohin Adamawa, Borno da kuma Yobe daga hannun mayakan wadanda suka yi kaka gida. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China