in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Uganda ta yaba da matakin Sin na goyon bayan shirin zaman lafiya a Sudan ta Kudu
2015-01-14 10:43:38 cri

Kasar Uganda ta nuna yabo kan matakin da kasar Sin ta dauka na tura tawagogin sojojin wanzar da zaman lafiya a kasar Sudan ta Kudu, da kuma nuna goyon bayanta kan kokarin shiga tsakani na kungiyar IGAD domin kawo karshen yake yake a cikin wannan kasa.

Asuman Kiyingi, ministan harkokin wajen kasar Uganda, ya shaida wa manema labarai a ranar Talata a birnin Kampala cewa, kasar Sin za ta dauki muhimmin matsayi a cikin shawarwarin bangarorin dake yaki da juna a Sudan ta Kudu, wato shugaba Salva Kiir da tsohon mataimakinsa Riek Machar da yanzu shi ne shugaban masu adawa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China