in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Uganda ta kaddamar da shirin yaki da cin hanci na shekaru 5
2014-12-10 10:24:56 cri

Kasar Uganda ta kaddamar a ranar Talata da wani shiri na shekaru biyar domin yaki da matsalar cin hanci dake kamari a cikin kasar, lokacin da ake tunawa da ranar kasa da kasa ta yaki da cin hanci.

A cewar Selon Simon Lokodo, ministan kasa kan bin doka, gwamnatin kasar ta bullo da wani shiri na shekaru biyar mai taken "dabarar kasa ta yaki da cin hanci domin karfafa yaki da cin hanci". Wannan dabara na samar da wani tsarin kasa domin aza hanyar siyasun gwamnati, tsare-tsare da ayyukan ma'aikatun gwamnati daban daban, jihohi, da ma gwamnatocin yankunan kasar baki daya wajen yaki da matsalar cin hanci.(Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China