in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Guinea-Bissau ta karyata batun cafke sojojin Gambiya dake hannu cikin yunkurin juyin mulki
2015-01-05 09:59:06 cri

Kasar Guinea-Bissau ta karyata batun cafke a cikin kasarta sojojin kasar Gambiya dake da hannu a yunkurin juyin mulki kan shugaban kasar Yahya Jammeh. Babu wani sojin kasar Gambiya da ya shigo kasar Guinea-Bissau, kuma jami'an tsaron kasar ba su cafke kowa ba, in ji gwamnatin Guinea-Bissau a cikin wata sanarwa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua ya samu kofinta a ranar Lahadi.

Gwamnatin Guinea-Bissau ta bayyana yin allawadai da yunkurin juyin mulkin da ya faru a kasar Gambiya, in ji wannan sanarwa.

Kungiyar kare hakkin dan adam ta kasar Guinea-Bissau ta bayyana a cikin wata sanarwa cewa, an cafke wasu sojojin Gambiya uku a kasar Guinea-Bissau. Haka kuma, kungiyar ta yi kashedin tusa keyar wadannan sojoji domin gudun kadda gwamnatin Yahya Jammeh da ba ta girmama 'yancin dan adam ta yanke musu hukuncin kisa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China