in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana ci gaba da tantance gawawwakin fasinjojin da suka mutu a cikin hadarin jirgin saman AirAsia
2015-01-01 16:29:00 cri
Gwamnan jihar gabashin Java a Indonesia Mista Soekarwo ya ce, gwamnati za ta ci gaba da bayar da dukanin hadin kan da ake bukata domin tantance gawawwakin fasinjojin da suka mutu a hadarin jirgin sama na AirAsia.

Jirgin saman mai lamba QZ8501 wanda ya tashi ne daga Indonesia a kan hanyarsa ta zuwa Singapore. Amma sai jirgin ya bace bayan minti 42 da tashinsa a ranar Lahadi. Daga baya sai aka gano jirgin ya yi hatsari.

A yau Alhamis an kai wasu gawawwaki domin tantance su zuwa wani asibitin 'yan sanda na Surabaya, hekwatar lardin Java dake yankin gabashin kasar Indonesia.

Kwamandan rundunar sojoji masu bincike da gano gawawwakin wadanda suka yi hadarin a jirgin, Mr Eko Wiratmoko ya ce rashin kyaun yanayi ya kawo tsaiko a wurin binciken.

Magatakardan MDD Ban Ki-moon ya mika ta'aziyarsa ga iyalan wadanda hadarin ya rutsa da su.

Wata sanarwar da ta fito daga kakakin magatakardan MDD ta mika godiya ga gwamnatocin da suka kawo dauki domin kaddamar da bincike na gano jirgin bayan da ya bace. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China