Rahotanni daga Yaounde, babban birnin kasar Kamaru sun nuna cewa, sojojin kasar sun yi nasarar hallaka fiye da mayakan kungiyar Boko Haram guda 40 a cikin wani taho mu gama da suke yi da juna a yankin nesa da arewacin kasar.
Kamar yadda ministan watsa labaran kasar Issa Tchiroma Bakary ya tabbatar a daren Lahadin, sai dai ya ce, daya daga cikin sojojin kasar ya rasa ransa a wannan gumurzu.
A bayanin da ya yi, mayakan sun kai hari ne a wurare da dama a yankin kwanakin baya da suka hada da Amchide, Limani, Makari, Chogori, Waza da Achigchia, duk wadanda ke kan iyaka da kasar Nigeriya.
Kafin nan, a safiyar Lahadin mayakan suka far ma Achigachia, abin da ya tilasta wa sojojin Kamarun ja da baya, daga baya kuma suka yi nasarar kwace garin bayan da sojojin samar suka kawo dauki da jiragen su.
Mayakan sun samu asarar mutanen su kwarai a Chogori, inda a nan kawai aka hallaka musu guda 34, in ji minista Issa Bakari. (Fatimah)