Gwamnatin kasar Chadi ta cimma wani shirin kundin yanke hukunci dake bayyana niyyar soke hukuncin kisa, a cewar wani sakamakon taron ministocin kasar da Hassan Sylla Bakari, ministan sadarwa kuma kakakin gwamnati ya fitar.
Hukuncin kisa za'a maye gurbinsa da na hukuncin zaman yari na rai da rai kamar wani matakin zama gidan yari ba tare da samun damar fitowa ba, in ji Sylla Bakari. Hukuncin kisa, ko da yake har yanzu yana aiki a kasar Chadi, amma ba'a aiwatar da shi ba yau da kusan shekaru ishirin da suka gabata. (Maman Ada)