Dan takarar jam'iyyar Nidaa Tounes, Beji Caid Essebsi, ya lashe zaben shugaban kasar Tunisiya zagaye na biyu tare da kashi 55,68 cikin 100 na dukkan kuri'un da aka jefa, in ji hukumar zabe mai zaman kanta ta kasar Tunisiya (ISIE).
Ban da haka kuma, 'dan takara, shugaban kasar mai barin gado Moncef Marzouki ya samu kashi 44,32 cikin 100, a cewar shugaban hukumar ISIE, Chafik Sarsar, a yayin wani taron manema labarai. Hukumar ISIE na da kwanaki uku gabanta yanzu kafin ta ba da sakamakon din din din na zaben shugaban kasar, wato lokacin jiran duk wasu koke koken da 'yan takarar biyu ka iyar gabatarwa babban kotun kasar. (Maman Ada