in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta tura jami'an kiwon lafiya zuwa Guinea-Bissau a kan Ebola
2014-12-17 10:34:29 cri

Wata kungiyar jami'an kiwon lafiya daga gundumar Sichuan dake kudu maso yammacin kasar Sin za ta tafi kasar Guinea-Bissau domin horas da jami'an kiwon lafiyan dake kasar a kan kariya daga cutar Ebola, kamar yadda hukumar kiwon lafiyar gundumar ta sanar.

Kungiyoyin da suka kasu kashi uku za su tashi a ranar Alhamis din nan kuma za su yi kwanaki 32 suna ba da horo a Guinea-Bissau ga jami'an kiwon lafiya kimanin 500.

Ya zuwa watan Oktoban wannan shekarar, kasar Sin ta tura jami'an kiwon lafiya da kuma likitoci 450 zuwa yammacin Afrika, ta kuma gina dakunan gwajin cututtuka da dakunan ba da jinya a yankin. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China