in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping zai je yankin Macau don taya murnar cika shekaru 15 da komawar yankin a kasar Sin
2014-12-15 14:13:39 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping zai kai ziyara a yankin Macau tun daga ranar 19 zuwa 20 ga wannan wata don halartar bikin taya murnar cika shekaru 15 da komawar yankin a kasar Sin da kuma rantsuwar kama aiki na gwamnatin yankin karo na 4.

Wannan ne karo na farko da shugaba Xi Jinping zai kai ziyara a yankin Macau bayan da ya hau kujerar shugabancin kasar Sin.

Bisa labarin da aka bayar an ce, wannan ziyara da shugaba Xi Jinping zai kai a yankin Macau na janyo hankali sosai a yankin, bangarori daban daban suna ganin cewa, wannan ziyarar Xi Jinping ta sheda kulawa da goyon baya da gwamnatin kasar Sin ta nuna wa yankin Macau. Sa'an nan suna maraba da zuwan shugaba Xi Jinping. Don haka, gwamantin yankin Macau za ta shirya jerin bukukuwa don taya murnar cika shekaru 15 da komawar yankin a kasar Sin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China