in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tunisia ta hana 'yan kasarta zuwa Libya saboda tashin hankali
2014-12-15 10:56:57 cri

Kasar Tunisia ta gargadi 'yan kasarta da su kauracewa bulaguro zuwa kasar Libya musamman saboda tashin hankali a kusa da kan iyaka kasar da Libya.

Wasu wadanda ake yin tashin hankalin a idanunsu sun ce, a ranar Lahadi an kashe wadansu 'yan kasar Libya guda 2 a kan iyaka ta Ras Jedir.

Rahotannin kafofin yada labarai sun ba da tabbaci cewar, sojoji masu biyayya ga janar Khalifa Haftar mai ritaya sun kai hari a Boukamech, garin dake kusa da kan iyakan Tunisia da Libya daga kudu maso gabashin kasar.

Wadanda aka yi abin kan idanunsu a garuruwan Ben Guerdane da Zarzis sun tabbatar cewar, sun ji karan fashewar wasu abubuwa da kuma karan faduwar bindiga mai linzami daura da kan iyaka na Ras Jedir.

A halin da ake ciki, yankin kan iyaka ya zamanto wurin kai hare-hare, kuma hakan ya sa hukumomin Tunisia daukar mataki na samar da dakaru a kan iyaka domin kare kan iyakar kasar. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China