in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jirgin ruwa da ya nutse a tafkin Tanganyika ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 126 a DRC
2014-12-15 10:31:08 cri

Wani jirgin ruwa dake dauke da mutane ya nutse a ranar Alhamis a tafkin Tanganyika, dake gundumar Katanga dake kudu maso gabashin DRC-Congo, tare da janyo mutuwar mutane 126, in ji Top Congo, wani gidan rediyo mai zaman kansa dake birnin Kinshasa. Kuma an ceto rayukan mutane 221, a cewar wannan majiya.

Har dai zuwa yanzu, hukumomin kasar ba su ba da wani adadi ba na wannan hadarin jirgin ruwan. Hadarin dai ya faru a ranar Alhamis da yamma tsakanin biranen Moba da Kalemie, wanda ake ganin nauyin jama'a da kayayyaki da kuma iska mai karfi dake kadawa su ne dalilin abkuwar wannan hadari.

A ranar 22 ga watan Maris na baya baya, mutane fiye da 200 suka mutu a yayin da wani jirgin ruwan dake dauke da 'yan gudun hijiran DRC-Congo ya nutse a tafkin Albert, dake kan iyaka tsakanin DRC-Congo da Uganda. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China