in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bai kamata a bata lokaci ba wajen kwance damarar 'yan tawaye a DRC
2014-11-06 14:15:28 cri

MDD ta kara nananta kiran da ta yi na kaucewa bata lokaci a wajen kwance damarar sa kai ta rundunar 'yan tawaye ta "Democratic Forces for the Liberation of Rwanda" wadanda a yanzu suke a jamhuriyar damokradiyyar Congo.

Kwamitin tsaron MDD mai mambobi 15 ya ce, bai kamata ba a samu jinkiri a wajen kwance damarar 'yan tawaye domin da ma yankin gabashin Afrika shi ne ya tsaida ranar da za'a kwance damarar dakarun na Rwanda nan da zuwa 2 ga watan Janairun shekarar badi.

Kwamitin tsaron ya fito karara ya bukaci da a dauki mataki na soji a kan 'yan tawayen wadanda suka yi taurin kai a wajen kwance damarar.

Yan tawayen wadanda yawancinsu 'yan kabilar Hutu ne sun tsallako daga kasarsu zuwa Congo bayan kisan kare dangin da aka yi a kasar ta Rwanda a shekarar 1994, kuma 'yan tawayen sun yi shela a watan Mayu a kan cewa, za su kwance damarar, daga nan sai gwamnatin damokradiyyaar Congo ta kebe ranar 9 ga watan Yuni domin kwance damarar saboda karancin wadanda suka mika wuya a wajen kwance damarar, sai kasashen Afrika a watan Yuli suka amince da a kara msu tsawon lokacin watanni shida na aje makamansu gefe guda, tare da kwance damartarsu ta soji. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China