in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Namibiya na daukar ma'aikatan lafiya domin taimakawa yammacin Afrika yaki da Ebola
2014-12-09 10:29:11 cri

Kasar Namibiya ta fara daukar ma'aikatan kiwon lafiya domin taimakawa kasashen yammacin Afrika dake fama da cutar Ebola.

Sakataren din din din na ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar Namibiya, mista Andrew Ndishishi ya sanar a ranar Litinin cewa, ma'aikatar kiwon lafiya na daukar malaman asibiti, kwararru kan cututtuka masu yaduwa, ma'aikatan ba da jinya, kwararrun dakunan bincike da sauran ma'aikatan lafiya a matakai daban daban domin amsa kiraye kirayen kungiyar tarayyar Afrika (AU) wanda ta bukaci kasashe mambobinta da su taimaka da jami'an kiwon lafiya domin yaki da annobar cutar Ebola. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China