in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Syria ta bukaci MDD da ta dauki mataki kan farmakin jirgin sama da Isra'ila take kaiwa a Damascus
2014-12-08 10:35:36 cri

Ma'aikatar harkokin wajen kasar Syria ta bukaci MDD da ta dauki matakai a game da hare-haren jiragen sama da kasar Isra'ila take kaiwa a kan wasu matsugunni 2 na sojojin Syria.

Wata majiya ta kamfanin dillancin labarai na Syria SANA, ta ce, ma'aikatar harkokin wajen Syria, a cikin wata takarda da ta rubutawa MDD ta ce, ya kamata a dau mataki kan Isra'ila, wacce bata boye manufofinta ba, kuma an gabatar da wannan takardar bayan awoyi kadan da wasu jiragen saman yaki na Isra'ila suka kai farmaki a wasu wurare biyu, ciki har da ofishin sojoji dake kusa da babban filin saukar jiragen sama na Damascus.

Ma'aikatar harkokin wajen ta ce, kamata ya yi a dauki duk matakan da suka dace domin haramtawa Isra'ila kara aiwatar irin wannan hari.

Tun farko kwamandan rundunar dakarun Syria ya ce, hare-haren da Isra'ilar ke kaiwa, yana nuni da hannun da Isra'ila take da shi wajen goyon bayan ta'addanci a Syria. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China