in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Senegal za ta sake bude iyakokinta na kasa da Guinea
2014-12-02 09:52:35 cri

Kasar Senegal za ta aike nan da dan lokaci mai zuwa da wata tawagar ministoci a Conakry domin nazarin hanyoyin sake bude iyakokinta na kasa tare da kasar Guinea, da aka rufe dalilin barkewar cutar Ebola, in ji talabajin din kasar Senegal a ranar Litinin.

Wannan matakin, an dauke shi ne a yayin wata ganawa a birnin Dakar tsakanin shugaban kasar Senegal Macky Sall da takwaransa na Guinea Alpha Conde.

Kasar Senegal, bayan wani umurni na kungiyar tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS), za ta sake bude iyakokinta na sama da na ruwa tare da kasashen da suka fi fama da cutar Ebola. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China