in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kenya za ta lalata kananan makamai 5000 da aka karbe ba bisa doka ba
2014-11-27 14:04:27 cri

Kasar Kenya ta shirya wani aikin lalata kananan makamai fiye da dubu biyar da ba bisa doka ba da aka karbe daga hannun mutane, in ji wani babban jami'i a ranar Laraba.

Ministan cikin gidan Kenya, Joseph Ole Lenku, ya bayyana cewa, wadannan makamai da aka kebe domin lalatawa, an kara su kan wasu makamai dubu biyar da aka jima da karbewa, kuma aka lalata a tsawon shekaru.

Niyyar kasar Kenya na bullo da hanyoyin warware matsalolin dake nasaba da tashin hankali yanzu. Mun yi imanin cewa, muna iyar hana tashe tashen hankali da yake yake, kare rayuwar jama'a da kuma bunkasa cigaban 'dan adam, in ji mista Lenku. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China