in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 45 suka mutu a harin kunar bakin wake a gabashin Afghanistan
2014-11-24 11:04:23 cri

A kalla mutane 45 ne suka mutu yayin da wasu 60 suka jikkata a ranar Lahadi da yamma bayan wani harin kunar bakin waken da aka kai wani filin wasan kwallon raga a garin Yahya Khel, dake gundumar Paktika dake gabashin kasar Afghanistan, a cewar hukumomin kasar.

Shugaban Afghanistan Mohammad Ashraf Ghani ya yi allawadai da babbar murya da wannan harin kunar bakin wake, wanda ya kashe fararen hula 45 da ba su ji ba su gani ba, tare kuma da jikkata wasu 60, in ji fadar shugaban kasar Afghanistan a cikin wata sanarwa.

Fashewar ta faru ne a lokacin wasan kwallon raga, a cewar sanarwar. Shugaba Ashraf Ghani ya ba da umurni ga hukumomin da abin ya shafa da su samar da jinya yadda ya kamata ga wanda suka ji rauni a wannan gundumar dake kan iyaka da Pakistan, in ji sanarwar. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China