in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An tabbatar da ingancin na'urar bincike kan iyakar Mali da Guinea domin yaki da Ebola
2014-11-24 10:30:33 cri

Na'urar bincike dake da manufar yin rigakafin cutar Ebola a yankin Kouremale, birnin dake kan iyaka tsakanin Mali da Guinea, na da inganci, a cewar faraministan kasar Mali, Moussa Mara, bayan ya kai ziyara aiki a wannan yanki a ranar Lahadi, a cewar wata majiya mai tushe.

A birnin Kouremale mai nisan kilomita 127 da birnin Bamako, kana kuma babbar hanyar shige da fice tsakanin kasashen biyu ne aka fara gano mutumiya ta farko mai dauke da cutar Ebola da ta shigo kasar Mali, kuma wata karamar yarinya ce 'yar shekaru biyu da cutar ta kashe a cikin watan Oktoba. A cewar sanarwar fadar faraministan kasar Mali, matakin da aka dauka a Kouremale na da inganci sosai, kuma na'urar tana aiki a ko da yaushe. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China