in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamata ya yi kwamitin sulhu na MDD ya yi kwaskwarima bisa ka'idar hadin kai
2014-11-13 15:00:19 cri
Mataimakin zaunannen wakilin Sin dake MDD Wang Min ya bayyana a ranar 12 ga wata cewa, kwaskwarimar da kwamitin sulhu na MDD ya yi tana shafar makomar MDD da kuma moriyar dukkan kasashe mambobin MDD, don haka kamata ya yi a yi kwaskwarimar bisa ka'idar hadin kai.

A wannan rana an gudanar da cikakken zama na babban taron MDD karo na 69, inda aka tattauna batun yiwa kwamitin sulhu na MDD kwaskwarima. A jawabinsa Wang Min ya bayyana cewa, kasar Sin tana goyon bayan shirin yiwa kwamitin sulhun kwaskwarima, a ganinta, ya kamata a yi kwaskwarimar bisa manufar kara samar da wakilci da ikon fada aji ga kasashe masu tasowa, musamman kasashen Afirka, sannan a kara shigar da yawan kasashe matsakaita da kanana mambobin MDD cikin kwamitin sulhu domin bada shawara da taka muhimmiyar rawa, a kokarin kiyaye manufofi da ka'idojin kundin tsarin MDD da kuma babbar ka'idar kula da dangantakar dake tsakanin kasa da kasa.

Ban da wannan kuma, Wang Min ya bayyana cewa, yayin da ake kokarin yin kwaskwarimar, akwai bukatar kasashe mambobin MDD su yi shawarwari da yin la'akari da juna, musamman kula da muradun kasashe matsakaita da kanana don neman cimma matsaya guda. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China