An zabi wata mutumiyar Botswana Matshidiso Moeti a matsayin darektan hukumar lafiya ta duniya mai wakiltar yankin Afrika, a yayin wani taro na kwamitin hukumar lafiya ta duniya WHO mai kula da yankin Afrika a Cotonou a jiya Laraba.
Wakilai daga kasashen Afrika 37 ne suka zabe ta daga cikin wakilan kasashe 47 dake halartar taron.
Ana sa rai malama Moeti za ta fara aiki daga ranar 1 ga watan Fabarairun shekarar badi. (Suwaiba)