Shugaban kasar Nijar Issoufou Mahamadou ya gana a ranar Talata da kwamandan din haddadiyar rundunar sojojin Amurka reshen nahiyar Afrika (AFRICOM), janar David Rodriguez.
Wannan ganawa, an yi ta ne a gaban idon ministan tsaron kasar Nijar, Mahamadou Karidjo, shugaban rundunar sojojin Nijar, janar Seini Garba, jakadan kasar Amurka dake Nijar, madam Eunice Reddick, tare da kuma mambobin runkunin sojojin AFRICOM.
Rukunin sojojin AFRICOM ya kasance mai tafiyar da harkokinsa cikin 'yanci tun daga ranar daya ga watan Oktoban shekarar 2008. (Maman Ada)