in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kashe mutane 30 a harin da aka kai a jihar Yoben Nigeria
2014-11-05 14:11:36 cri

A kalla yayan kungiyar musulunci ta Shi'a 30 ne suka rasa rayukansu a sakamakon wani harin kunar bakin wake, da aka kai a kan yayan kungiyar Shi'a, a yayin da suke tafiya a cikin jerin gwano a Potiskum na jihar Yobe dake arewa maso gabashin Nigeria.

Sakataren zartaswar hukumar gudanarwa ta asibitocin jihar Yobe Mamman Mohammed ya ce, kawo ya zuwa yanzu an tabbatar da mutuwar mutane a kalla 30, kana wasu mutane 89 sun samu raunuka.

Sakataren zartaswar ya bayyana hakan ne a yayin da yake yin bayani ga gwamnan jihar Yobe Ibrahim Gaidam, wanda ya kai ziyara ga wadanda harin ya rutsa da su a babban asibitin Potiskum, kuma ya ce, kawo ya zuwa yanzu wadanda suka samu munanan raunuka, an tura su zuwa wasu asibitoci dake wajen Potiskum a Azare da Nguru.

Gwamnan na jihar Yobe ya ba da umurnin da a bai wa wadanda harin ya rutsa da su kulawa kyauta, a inda ya bayyana cewar, gwamnati za ta biya duk kulawar da za'a yi musu.

Gwamnan ya mika ta'aziyarsa ga kungiyar musulmi ta Shi'a reshen jihar Yobe. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China