An labarta cewa, ofishin jakadancin kasar Sin da ke kasar Saudiya da kuma karamin ofishin jakadancin kasar Sin da ke Jeddah sun taimakawa alahazan kasar Sin wajen gudanar da aikin hajjinsu cikin nasara, shugabannin ofisoshin sun ziyarci musulman kasar Sin da suka halarci aikin hajji na bana a Mekka. Bayan haka kuma, manyan kamfanonin jiragen sama uku na kasar Sin sun aika da jiragen sama 94 domin yin jigilar musulmai daga Beijing, Urumchi, Lanzhou, Yinchuan da Kunming zuwa Mekka da kuma dawo da su gida lafiya. (Tasallah)