in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Magatakardan MDD ya jinjinawa zaben da aka gudana a Tunisia
2014-10-28 10:52:36 cri

Magatakardan MDD Ban Ki-moon ya yiwa kasar Tunisia murna ta gudanar da zaben majalisar dokokin kasar, a inda ya ce, zaben wani babban mataki ne a game da makomar kasar.

Ban ya bayyana a cikin wata sanarwa cewar, zaben majalisar dokokin kasar wanda aka gudanar ranar Lahadin da ta gabata, ya zamanto wata rana ta tarihi a game da komawa ga kan tsarin damokradiyya a kasar.

Ban ya kara da cewar, zaben ya haifar da dimbin fata na gari, to amma ya ce, har yanzu akwai manyan ayyuka a gaban gwamnatin kasar ta gaba.

A ranar Alhamis mai zuwa ne za'a bayyana sakamakon zaben na farko kuma MDD ta ce a shirya take ta tallafawa kasar ta Tunisia wadda kuma tuni ta shirya gudanar da zaben shugaban kasa a ranar 23 ga watan Nuwumba mai zuwa. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China