in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bukaci Afrika da ta gudanar da gyare-gyare a bangaren hayar gidaje
2014-10-15 15:04:02 cri

Majalisar dinkin duniya ta bukaci a ranar Talata, kasashen Afrika da su gudanar da gyare-gyare a bangaren haya, ta yadda za'a canja bunkasuwar unguwannin talakawa a yankunan birane.

Claudio Acioly, darektan reshen cigaban karfin MDD da muhallin jama'a, ya bayyana a yayin taron shiyya kan haya a Nairobi cewa, bunkasuwar unguwannin talakawa na tafiya daidaita da cigaban birane cikin sauri. Akwai manufofin siyasa dake ingiza wasu tsare-tsaren ba da haya da cinkoson jama'a cikin gidaje, in ji mista Acioly a yayin bikin rufe taro kan haya a Afrika, da aka kwashe kwanaki biyu ana yinsa wanda kuma ya hada masu ruwa da tsaki a bangaren haya a Afrika, domin tattauna cigaban kasuwannin haya bisa doka.

Mista Acioly ya bayyana cewa, manufofin siyasa a wannan fanni ya kamata a fadada manyan bukatu, ba da haya, farashi da ka'idodi da matakai a wannan fanni da sauransu. Haka kuma da kirkiro manufofin haya, tare da manufofin tsara birane, ta yadda za'a iyar cike karancin gidajen haya. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China