in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sama da mutane miliyan 1 na fuskantar barazanar yunwa a Somaliya
2014-10-15 10:44:57 cri

Manzon musamman na MDD a Somaliya Nicholas Kay, ya yi gargadin cewa, akwai sama da mutane miliyan 1 da ba su da abin saka wa a bakin salati, duk da ci gaban da aka samu a kasar a bangaren siyasa da tsaro.

Jami'in na MDD ya bayyana hakan ne yayin da yake yiwa kwamitin sulhu na MDD bayani game da yanayin da ake ciki a kasar da ta shafe tsawon lokaci tana fama da rikici.

Mr. Kay ya ce, duk da galaban da aka samu a kan kungiyar Al-Shabaab, akwai bukatar gwamnatin kasar da abokan huldarta na ketare su dauki matakan da suka dace cikin gaggawa a bangaren tsaro, ci gaba, bangarorin siyasa da jin kai.

Bugu da kari wajibi ne a dama da mata da matasa cikin matakan sulhunta al'ummomin kasar tare da kafa gwamnatocin shiyyoyi na wucin gadi.

Daga karshe yana fatan za a bullo da wata sabuwar taswirar tarayyar Somaliya ya zuwa karshen wannan shekara tare da hanzarta kafa hukumar zabe mai zamanta da kuma hukumar shata kan iyaka. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China