in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnan jihar Kano zai shiga zaben shugaban kasar Najeriya
2014-10-14 15:17:45 cri

Gwamnan jihar Kano dake arewa maso yammacin Najeriya, Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana cewa, zai shiga zaben shugaban kasa na shekarar 2015, in ji daya daga cikin manyan na hannun daman gwamnan a ranar Litinin.

Mista Kwankwaso, wanda a da yake mamba na jam'iyyar PDP mai mulki, ya bayyana niyyarsa a ranar Alhamis na shiga zaben shugaban kasa a matsayin 'dan takarar babbar jam'iyyar adawa ta APC a Najeriya, wato sabuwar jam'iyyarsa, in ji Olisaemeka Akumaki, darektan cibiyar yakin neman zabe na gwamnan a gaban manema labarai a birnin Abuja. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China