in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Sin ya tashi zuwa Jamus, Rasha da Italiya domin fara ziyarar aiki
2014-10-09 14:43:07 cri

A ranar Alhamis din nan 9 ga wata, firaministan kasar Sin Li Keqiang ya tashi daga nan birnin Beijing zuwa kasashen Jamus, Rasha da Italiya a wani ziyarar aiki daga wannan rana zuwa 17 ga watan nan da muke ciki.

A lokacin ziyararsa a Jamus, ana sa ran zai jagoranci tattaunawa karo na uku tsakanin gwamntocin kasashen biyu, shi da shugaba Angela Merkel. A kasar Rasha kuma, zai halarci taro na a kai a kai karo na 19 tsakanin shi da takwaransa Dmitry Medvedev.

Bisa gayyatar Jose Graziano da Silva, babban darekta a ofishin samar da abinci da aikin gona na MDD wato FAO, firaminista Li zai ziyarci cibiyar ofishin a birnin Rome dake Italiya.

Har ila yau, firaministan na kasar Sin zai halarci taron shugabanni karo na 10 na Asiya da yankin Turai da shi ma za'a yi a Milan bisa gayyatar shugaban kungiyar tarayyar Turai Herman Van Rompuy, firaministan Italiya Matteo Renzi da kuma shugaban kwamitin tarayyar Turai Jos Manuel Barroso. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China