in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi kira da a mutunta cikakkun yankunan kasa
2014-09-11 20:44:01 cri
Kakakin ma'aikatan harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta yi kira da a rika mutunta 'yanci da cikakkun yankunan kasashe.

Madam Hua ta bayyana hakan ne yau Alhamis yayin da shugaban Amurka Barack Obama ya lashi takwabin kaddamar da hari ta sama a kasashen Iraki da Syria inda ta ce, kamata ya yi a martaba dokokin kasa da kasa game da yaki da ta'addanci.

Hua ta ce, yakin da ake da ayyukan ta'addanci a duniya a halin yanzu batu ne mai sarkakiya, don haka take fatan kasashen duniya za su hada kai da kasashe da abin ya shafa a kokarin da suke na dawo da doka da oda cikin hanzari da sulhuntawa, zaman lafiya da ci gaban.

Ta ce, wannan mataki zai taimaka wajen kawar da karuwar ayyukan ta'addanci a wadannan wurare ta yadda za a samu dauwamammen zaman lafiya da kwanciyar hankali a shiyyar.

Madam Hua ta ce, kasar Sin a shirye take ta martaba ka'idar mutunta juna, nuna daidaici da hadin kai don karfafa hadin gwiwar yaki da ta'adanci tare da sauran kasashen duniya da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya baki daya. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China