in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin tsaron MDD ya yi Allah wadai da kisan ma'aikatan wanzar da zaman lafiya a Mali
2014-09-03 15:33:37 cri

Kwamitin tsaron MDD ya bayyana matukar takaici game da wani harin bam, wanda ya haddasa rasuwar jami'an tawagar wanzar da zaman lafiya ta MINUSMA, 'yan kasar Chadi su 4 a arewacin Mali.

Cikin wata sanarwa da kwamitin ya fitar a ranar Talata, daukacin wakilansa 15 sun mika sakon ta'aziyar su ga iyalai da gwamnatin kasar Chadi, bisa rasuwar ma'aikatan, tare da fatan samun sauki ga wadanda harin ya jikkata.

Kaza lika sanarwar ta bukaci mahukuntan kasar Mali da su gudanar da bincike kan wannan lamari, da nufin gurfanar da wadanda ake zargi da aikata wannan ta'asa gaban kuliya. (saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China