in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU da MDD sun dau alkawarin taimakawa kasashen dake yankin tabkunan Afrika
2014-08-28 09:49:11 cri

Kungiyar tarayyar kasashen Afrika AU tare da MDD gaba daya sun dau alkawarin nuna hadin kansu domin karfafa hadin gwiwwa da kasashen dake yankin tabkuna.

Madam Nkosazana Dlamini-Zuma, shugabar kungiyar AU ta sanar da hakan a ranar Talatan nan lokacin da ta gana da sabon manzon musamman na MDD a yankin tabkunan nahiyar, Said Djinnit a cibiyar kungiyar dake birnin Adis Ababa na kasar Habasha, kamar yadda sanarwa daga kungiyar ta bayyana.

Said Djinnit ya kuma tattauna da kwamishinan kungiyar a bangaren zaman lafiya da tsaro Smail Chergui, wanda a lokacin tattaunawar suka mai da hankali a kan hanyar da za a samar da taimako ga kokarin sauran kasashen duniya a wannan shiyyar domin tabbatar da zaman lafiya, tsaro da hadin gwiwwa a jamhuriyar demokradiyar Kongo, da ma yankin baki daya domin a samu nasarorin da aka gani cikin 'yan watannin nan ya inganta.

Hukumomin biyu sun jaddada bukatar da ke akwai ta inganta tare da karfafa tabbacin a tsakanin kasashe na wannan yankin, a kammala ayyukan wargaza duk wassu rundunar masu dauke da makamai ba bisa ka'ida ba, a mai da hankali yadda ya kamata a kan tattalin arziki da ci gaba a wannan tsari da ake son cimmawa na zaman lafiya, tsaro da hadin gwiwwa. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China