in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen yammacin Afrika za su shirya taron ministoci kan cutar Ebola
2014-08-26 10:27:36 cri

Wata guda kacal bayan taron shawarwari na farko domin fuskantar annobar cutar Ebola, ministocin kiwon lafiya na kungiyar cigaban tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS) za su sake shirya wani sabon taro a ranar Alhamis mai zuwa domin tattauna matakan yaki da cutar Ebola da ta yi sanadiyyar mutuwar mutane dubu daya da dari hudu tun daga cikin watan Febrairu. Wannan taron gaggawa zai biyon bayan wani taron kwararrun kiwon lafiya na tsawon kwanaki biyu wato a ranakun Laraba da Alhamis, a cewar wata sanarwar ma'aikatar kiwon lafitar kasar Ghana. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China