in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An tabbatar da mutuwar mutane 2 sakamakon cutar Ebola a DRC
2014-08-25 10:37:02 cri

Ministan lafiya na jamhuriyar damokradiyyar Congo DRC Felix Kabange Numbi ya bayyana cewar, wasu mutane biyu sun mutu a sakamakon cutar Ebola a garin Djera, wanda ke yankin arewa maso yammacin gundumar Equateur na kasar da ke yankin tsakiyar Afrika.

A yayin da ministan ke jawabi ta kafar gidan talabijin na kasar, ya kara da cewa, a wannan watan na Agusta, an samu barkewar ciwon zazzabi da ba'a gane irinsa ba a yankin Equateur, wanda ya yi sanadiyyar rasuwar mutane 13, kuma daga cikin wasu mutane takwas da ke fama da zazzabin, an gano cewar, 2 daga cikin su suna dauke da kwayar cutar Ebola mai saurin kashe bil'adama.

Amma kuma ministan ya ce, a halin da ake ciki kasar ta samu nasarar dakilar da barkewar cutar ta Ebola a yankin Djera, a inda kuma ya yi kira ga al'ummar yankin da su kwantar da hankalinsu.

Ministan Lafiyar ya ce, kamuwar mutane biyu da aka gano a yankin ba ya da nasaba da barkewar cutar Ebola ta yankin Afrika ta yamma, wanda ya kawo ya zuwa yanzu ya haddasa mutuwar mutane sama da 1,400. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China