Hakan dai na kunshe ne cikin wata sanarwar da ma'aikatar ta fitar, wadda ta ce za a tsagaita bude wutar ne a Litinin din nan, koda yake hakan bai shafi yankunan kewayen birnin Rafah dake kudancin Gaza ba.
Kaza lika Isra'ila za ta maida martani kan duk wani hari da aka kai mata a wannan tsakani. (Saminu)